Connect with us

News

Rikicin Sudan: Sama da mutane dubu 20 suka tsallaka zuwa Chadi

Published

on

DAGA YADIR SANI ABDULLAHI 

 

 

Hukumar abinci ta duniya ta ce hukumomin Chadi hade da kungiyoyin agaji na bukatar tallafin gaggawa domin taimakawa dubban masu gudun hijira dake tsallakawa daga sudan dake makotaka da kasar.

 

Majalisar dinkin duniya ta ce akalla mutane dubu 20 ne suka tsallaka Sudan zuwa Chadi tun bayan barkewar rikici tsakanin rundunar sojin kasar da dakarun kai daukin gaggawa a farkon watan nan na Afrilu.

Advertisement

 

Darektan hukumar a Chadi, Pierre Honnorat na cewa bukatar ta yi tsanani sosai domin nan da makonni 6 ko 8 masu zuwa ba za su iya kai wa yankunan da masu gudun hijirar suke dauki ba saboda yanayi na ruwan sama.

Shin kun taɓa fuskantar dannau yayin bacci?

Tun a farkon makon nan aka soma rabawa ‘yan gudun hijiran da suka isa kan iyakar Adre abinci da sauran kayakin jinkai.

 

Rikicin da aka shafe sama da makonni 2 ana yi ya mayar da Khartoum tamkar filin daga, sannan ya jefa illahirin Kasar cikin halin kaka-ni-kayi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending