Business
CBN Ya Dage Takunkumin Daya Sanyawa Asusun Masu Ajiyar Kudin Waje
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Babban bankin kasa CBN ya dage dokar da aka sanya wa asusun masu ajiyar kudaden waje.
A cikin wata sanarwa da CBN ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata, sabuwar dokar ta bai wa masu asusun ajiyar kudi damar yin ajiya kyauta, ba tare da kayyade kudaden shiga a cikin asusun ba, da kuma fitar da kudi har dala 10,000 a kullum.
Jaridar PUNCH ta samu a shekarar 2021 ta bayyana cewa, “Mafi girman kayyade chanjin kudin kasashen waje ta hanyar ajiya a yanzu shine $5,000 a kowane wata.
Johann Rupert na Afirka ta Kudu ya zarce Aliko Dangote a matsayin wanda ya fi kowa kudi a Afirka
Sai dai babban bankin na CBN ya takaita wannan iyaka ne biyo bayan wani taron kwamitin ma’aikatan bankin da aka gudanar domin tattauna yadda ake aiwatarwa da kuma tasirin sauye-sauyen manufofin ga al’ummar bankuna.
A cewar CBN, canje-canjen manufofin suna da nufin haɓaka gaskiya, daidaito, da kuma gano farashi a cikin kasuwar canjin kudi, don ingantasu
An bukaci bankunan da su tabbatar da hanzarta aiwatar da duk wasu ma’amaloli marasa shinge a madadin abokan cinikinsu
