Connect with us

News

Hukumar EFCC Ta Saki Ortom Bayan Sa’o’i 10 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

An saki tsohon gwamna Samuel Ortom na jihar Benue daga hannun hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC.

Advertisement

Jaridar daily trust ta ruwaito yadda tsohon gwamnan ya amsa gayyatar hukumar da misalin karfe 10:00 na safiyar ranar Talata.

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Cire Kudaden Yan Fansho

Ya shiga cikin ofishin shiyya na Makurdi na hukumar, wanda ke kan titin Alor Gordon a babban birnin jihar, tare da rakiyar wasu tsoffin IDES dinsa guda biyu.

Advertisement

Mataimakin tsohon gwamnan kan harkokin yada labarai, Terver Akase, da kuma babban mataimakin na musamman kan ayyuka na musamman, Abraham Kwanhgu, an gansu tare da shi.

Jami’an ‘yan sanda sun gana da Ortom kan kashe kudaden da Benue ta yi a karkashinsa.

Advertisement

Daya daga cikin masu taimaka masa, wanda bai so a ambaci sunansa ba, ya shaida wa manema labarai a wajen ginin hukumar cewa babu wani abin fargaba.

A yayin zaman majalisar ministocinsa da aka gudanar a tsohon dakin liyafa na gidan gwamnati, Makurdi, Ortom ya bukaci ‘yan majalisarsa da kada su ji tsoro a duk lokacin da EFCC ta gayyace su don amsa tambayoyi.
Ortom ya shaidawa mambobin majalisar ministocinsa cewa shi ba matsoraci ba ne da zai gudu daga EFCC.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending