Connect with us

News

Tinubu Ya Gana Da Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya gana da tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu da tsohon sakataren jam’iyyar Iyiola Omisore da suka sauka daga kan kujerunsu, a fadar shugaban kasa dake Villa Abuja.

Advertisement

Mutanen biyu  sun je  fadar shugaban kasar  ne a tare, Kuma  an gansu suna  cikin annushuwa  bayan  kammala  zaman da karfe  1 da rabi na rana,  batare  da sun gana  da manema Labarai ba.

Abin takaici ne yadda ake samun ƙaruwar Matasa dake shaye shaye – Sarkin Kano

Sai dai rahotanni sun baiyana cewar  ziyarar tasu bata rasa nasaba da  rikicin cikin gida  na jam’iyyar  wanda  yasa  mutanen biyu sauka daga kan mukamansu a makon jiya.

Advertisement

Kazalika  a ranar Litinin din makon jiya an aiyana mataimakin shugaban jam’iyyar  mai kula da shiyyar  Arewa  Sanata Abubakar Kyari a matsayin mukaddashin shugabanta, jim kadan bayan kammala zaman kwamitin gudanarwar  jam’iyyar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending