Connect with us

News

Tinubu Yace Za Su Kara Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa na duba yiwuwar kara mafi karancin albashin ma’aikata.

Advertisement

Tinubu ya fadi haka ne a jawabin da ya yi wa ’yan kasa a Yammacin wannan Litinin din.

Cikaken Jawabin Shugaba Tinubu a daren Yau litinin

“Karin albashi na nan tafe,” a cewarsa.

Advertisement

“Da zarar mun daddale game da mafi karancin albashi da kuma sauran abubuwa, za mu saka shi cikin kasafin kudi domin fara aiki cikin gaggawa.

“Tuni mun kaddamar da tsarin sake duba albashin ma’aikata.”

Advertisement

Haka kuma a jawabin nasa, Tinubu ya ce gwamnatinsa ta dauki tsauraran matakai ne saboda sun zama dole, “kuma babu waɗanda suka fi su sauki.”

“Da a ce akwai hanyoyin da suka fi su sauki da na bi,” in ji shi.

Advertisement

“Abin da zan iya yi kawai shi ne daukar matakan da za su saukaka yanayin.

“Gwamnatina za ta tabbatar da yin aiki tare da dukkan jihohi don rage radadin da ’yan kasa ke ji.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending