Connect with us

News

Kotu Ta Tsare Wani Matashi A Kan Zargin Satar Tunkiya A Jahar Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Wata kotun shari’a a jihar Kano a ranar Talata ta bayar da umarnin tsare wani matashi dan shekara 29, a gidan gyaran hali kan zargin satar wata tunkiya da ta kai Naira 27,000.

Advertisement

Ana tuhumar matashin da ke zaune a Sani Manage Quarters a Jahar Kano da laifin satar.

An Sake Samun Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Adamawa

Alkalin kotun, Malam Umar Lawal-Abubakar, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 28 ga watan Satumba.
Tun da farko, dan sanda mai gabatar da kara, Insp Abdullahi Wada, ya shaida wa kotun cewa wani mutum mai suna Sabo Iliyasu, ne ya shigar da kara, ya kai karar ne a ranar 11 ga watan Satumba a ofishin ‘yan sanda na Mandawari.

Advertisement

Wada ya ce wanda ake tuhumar ya kutsa cikin rumfar wanda ake zargin da ke unguear Sani Mainage ya sace masa Tunkiya daya.

Ya lura cewa wanda ake tuhumar ya kai Tunkiya zuwa wani ginin kwango da ba a kammala ba ya yanka.

Advertisement

Lokacin da aka karanta wa wanda ake tuhuma tuhumar, ya musanta aikata laifin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending