News
Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bayan Surfawa Shugaban Kasa Ashar
Kotu ta yanke wa wani mutum hukuncin kisa kan zagin Shugaban Tunisiya Kais Saied da kuma yada farfaganda kan tsaro.
Mutumin da hukumomin Tunisiya suka sakaye sunansa an yanke masa hukunci kan zargin aikata laifuka guda uku da suka hada da barazanar hambarar da gwamnati wanda ke kasancewa cin amanar kasa da zagin Shugaba Saied da kuma yada labaran karya a kafafen sada zumunta.
Da yake yanke hukunci kan laifin da mutumin ya aikata, alkalin kotun ya sanar da cewa laifin da mutumin mai shekaru 51 ya aikata yaci karo da kundin tsarin mulkin kasar da aka yi wa kwaskwarima a 2022, musamman dokar nan mai lamba 54 da tayi hani kan yada kamalan kiyayya a Intanet.
Tun bayan hawansa kan karagar mulkin kasar ta Tunisiya, hukumomin kasar sun daure mutane da dama ciki har da ‘yan adawa da masu fafutukar kare hakkin bil Adama da manema labarai da dai sauransu.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion5 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
