Interview
Ba iya karatu muke koyar da Dalibai ba har da zamantakewar Yau Da Kullun -Dakta Sabo Wada Dutse.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban kwalejin kimiyya da fasaha ta Hussaini Adamu Dake kazaure a jihar jigawa Dakta Sabo wada Dutse, yace ba’a iya karatun boko suke koyar da Dalibai ba harda yadda zasuyi mu’amulla da juna tare da kulawa da tarbiyyar Daliban kwalejin kasancewar kwalejin ta hada mutane daga jihohi maban banta a addini da yare dakuma alada na fadin Najeriya.
Ya bayyana hakan ne a yayin zantawarsa da manema labarai a ofishinsa dake kwalejin kimiyya da fasaha ta Hussaini Adamu Dake kazaure
Haka kuma yace “Duba da kwalejin na karkashin gwamnatin tarayya Dukkanin Daliban kasarnan nada damar neman Gurbin karatu a kwalejin a shirye muke tsaf wajen bada gurbin karatu a kwalejin domin karantar ilimin kimiyya da fasaha wanda idan har Dalibi yakaranta to babu shakka zai iya dogara dakansa batare da yajira aikin gwamnati ba ko kuma wani Dalibi nada damar amfani da iliminsa na kimiyya wajen gudanar da sana’oi iri iri domin ka samu ingantacciyar rayuwa”.
Jaridar Inda Ranka ta rawaito cewa Dakta sabo wada yakara da cewar “Ina janhankali ga Daliban wannan makarata dasu zamo masu mutumta juna dukda banbancin yare da addini da kuma alada kowa yake mutumda addinin kowa kada Dan Arewa yake kyamatar Dan kudu ko Dan kudu yake kyamatar Dan Arewa mudauka cewar tunda karatu yahada mu to muzamo tsintsiya daya madauri daya.
Sannan Ina kara jan hankalin Dalibai dasu mayarda hankali wajen karatunsu domin ilimi shine jigon rayuwa duba da mashimmancin sa ga rayuwar mu, kada Makaranta tazamo gurin da muke aikata badai dai ba muyi amfani da lokacin mu wajen ginawa kan mu gobe mai kyau, kada muzamo masu cin amanar iyayen mu akan abinda suka turomu mu koya.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
