Connect with us

Sports

Senegal ta ba da hutun aiki don murnar lashe kofin Afcon

Published

on

FB IMG 16442243928203916

Daga kabiru basiru fulatan

Shugaban Senegal Macky Sall ya ayyana Litinin a matsayin ranar hutun aiki don ci gaba da murnar lashe Kofin Ƙasashen Afirka (Afcon 2021) da tawagar ƙasar ta yi ranar Lahadi da dare a Kamaru.

Advertisements
Advertisements

Shugaban wanda yanzu ba ya cikin ƙasar, ya soke taƙaita balaguron da yake yi domin tarɓar taurarin ‘yan wasa nasa.

Advertisements

Shugaba Sall zai bai wa tawagar kyauta ta musamman ranar talata a fadarsa, a cewar kafar yaɗa labaran ƙasar ta RTS.

Advertisements
Advertisements

Senegal ta lashe kofin Afcon a karon farko a tarihi bayan ta buga wasan ƙarshe har sau biyu a baya – a 2019 da 2022.

Sun doke tawagar Egypt ne mai Mohamed Salah 4-2 a bugun finareti bayan an tashi wasa 0-0.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending