News
Isra’ila da Hamas sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta na wucin-gadi
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Isra’ila da Hamas sun tabbatar da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta wucin gadi, inda Hamas za ta sako ‘yan Isra’ila 50 da take garkuwa da su, dukkansu mata da kananan yara.
Cikin wata sanarwar da Hamas ta fitar, ta yi ƙarin bayani kan cewa Isra’ila za ta saki Falasɗinawa matasa da mata 150 da ake tsare da su a gidajen yarin Isra’ila.
Wakiliyar BBC ta ce jami’an Isra’ila sun ce an cimma yarjejeniyar dakatar da wuta ta kwanaki huɗu.
A tsakanin kwanakin ne za a miƙa Isra’ilawa 50, idan komai ya tafi daidai za a tsawaita dakatar da buɗe wutar da ƙarin kwanaki uku.
Qatar – wadda ta shiga tsakani – ta ce nan da sa’o’i 24 za a sanar da lokacin fara aikin yarjejeniyar.
A wani labarin kuma Shari’ar gwamna: Al’umma da dama sun shiga rudani a jihar kano sakamakon fitar hukuncin kotun daukaka kara
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
