Connect with us

News

SERAP Ta Bukaci Bankin Duniya Ya Dena Bawa Jihohin Kasar Nan Bashi

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

kungiyar nan mai rajin tabbatar da adalci a hukumomi da ma’aikatun gwamnati SERAP, ke yin kira ga bankin duniya da ya dakatar da baiwa jihohin kasar nan 36 lamuni, saboda zargin karkatar da kudaden da suke yi

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan kungiyar Kolawole Oluwadare ya fitar a ranar lahadi.

Gwamnatin Tarayya Zata Karya Farashin Makamashin Iskar Gas A Fadin Kasar Nan 

Wasikar mai dauke da kwananann wata 25 ga watan da muke ciki, ta bukaci bankin duniya da ya gudanar da bincike kan yadda aka kashe kudin da ya bayar a matsayin bashi da gwamnonin kasar nan suka karbo daga hannunsa, sannan ya dena bayar da bashin matukar ya gano akwai lauje cikin nadi a bada bashin.

Kungiyar ta ce akwai bukatar bankin duniyar ya dena baiwa jihohi bashi har sai sunyi cikakken bayani na gamsarwa kan yadda suka kashe sauran basussukan da suka karba daga wajensa.

Advertisement

 

Awani labarin kuma Gwamnatin Tarayya Zata Karya Farashin Makamashin Iskar Gas A Fadin Kasar Nan 

Gawurtacciyar guguwa haɗe da ruwan sama sun auka wa kudancin ƙasar Ukraine, lamarin da aka jima ba a gani ba cikin shekaru a yankin Tekun Baharul Aswad.

Kusan mutum dubu biyar da ke yankin Crimea wanda Rasha ta mamaye na zaune ba tare da wutar lantarki ba, bayan guguwar ta karya manyan bishiyoyin da suka faɗa kan turakun wutar lantarki.

Guguwar ta kuma janyo ambaliyar ruwa a kauyuka da garuruwan da ke kusa, an kuma kwashe mazauna garin Sebastopol bayan ambaliyar da kogin yankin ya yi.

Hotunan da aka yaɗa a intanet sun nuna biranen Bed-yansk da Mariupol da Tekun Azov duk ruwa ya mamaye.

Advertisement

A can yammacin birnin Odesa ma lamarin ya yi muni.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending