News
Yadda ‘yan bindiga sace lodin makaɗa, mawaƙi, ‘yan rawa, ‘yan amshi da sanƙira
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Fitaccen mawaƙin ‘balaja’u’, rawar kwambilon da aka fi sani da kiɗan juju, Omoba De Jombo, ya faɗa hannun ‘yan bindiga, shi da ɗaukacin tawagar sa kakaf.
Sauran waɗanda aka yi garkuwar tare da shi, sun haɗa da dukkan tawagar da suka haɗa da ‘yan rawa, ‘yan amshi har ma da sanƙira.
Hausawan Jihar Ogun Na Zanga-zangar Neman Tabbatar Da Adalci A Shari’ar Gwamnan Kano
An kama su ne kan hanyar su ta zuwa Kogi daga Abuja domin zuwa raƙƙashewa a Jihar Kogi.
Waɗanda suka yi garkuwa da su dai sun ce ba za su sake su ba sai an biya diyyar Naira miliyan 10 kan kowane mutum ɗaya.
Wani mawaƙi ne mai suna Adeyinka Adeboye ya fara watsa labarin yin garkuwa da tawagar ɗan uwan sa mawaƙin a shafin sa na Instagram, lamarin da ya ja hankulan jama’a da dama.
Boyebest ya ce masu garkuwar sun bugo waya, sun nemi a biya diyyar Naira miliyan 10 kan kowane mutum ɗaya.
Abokan sana’ar sa dai na ci gaba da muna damuwa da kuma addu’ar neman kuɓutar su.
Ya ce an kama su ne kan hanyar su bayan sun dawo daga Jihar Ondo, inda suka je suka yi wasa.
Wani mai suna Aysneakey ya bayyana cewa cikin waɗanda aka yi garkuwar da su, akwai ɗan’uwan sa ɗaya.
Ya ce an kama su ne tsakanin titin Obajana/Kabba.
Sai dai kuma ba a bayyana yawan waɗanda aka yi garkuwar da su ba. Kuma ba a bayyana jinsin ‘yan bindigar da suka arce da su ba.
Premium Times ta ruwaito cewa Haka kuma har zuwa yanzu ba a san shin har da kayan kiɗan aka haɗa aka nausa cikin daji da su ba, ko kuma a cikin mota aka bar kayan kiɗan.
A wani labarin kuma Hausawan Jihar Ogun Na Zanga-zangar Neman Tabbatar Da Adalci A Shari’ar Gwamnan Kano
Yanzu dai Babu wani Abu da al’ummar jihar kano ke yawan tattaunawa akansa Kamar batun shari’ar zaben gwamnan jihar.
Wakilin jaridar Inda Ranka Yasir Sani Abdullahi ya gano yadda kusan da yawa daga cikin wuraren zaman alumma da kasuwanni harma da ofisoshin gwamnatin da masu zaman Kansu, Babu wani batu da yafi daukar hankali Kamar batun shari’ar
Magoya bayan dukkan babgarorin manyan jam’iyyun APC Dana NNPP na bugar kirgin samun nasara a kotun koli.
Jam’iyyar APC na da kwarin guiwar cewa Zata Kara samun nasara a kotun koli kasancewar kotun farko da ta biyu duka ta Bata nasara
Sai dai jam’iyyar NNPP Bayan korafe korafe da tayi akan hukunce hukunce na kotun baya, yanzu ta bayyana kwarin guiwar da take dashi na samun nasara a kotun koli.
Al’ummar jihar kano da dukkan bangarorin manyan jam’iyyun APC Da NNPP na dakon hukuncin na karshe na kotun koli wadda ake saran Zata yanke cikin karshen watan Nan, shi zai kawo karshen jayayya da kowane bangare keyi a jihar kano.
Masu iya magana na cewa Shari’a mace ce da ciki ba’asan wa Zata Haifa ba.
