Connect with us

Sports

Aljeriya Ta Kori Kocinta Bayan Cire Ta A Gasar Cin Kofin Afrika.

Published

on

DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO

A ranar Laraba Aljeriya ta kori kocinta, Djamel Belmadi, bayan da aka fitar da ita daga Gasar Cin Kofin Afrika.

Advertisement

Aljeriya ta dauki wannan mataki a kan Belmadi ne bayan da ta sha kashi a hannun Mauritania a ranar Talata a wasansu na karshe na rukuninsu a Ivory Coast.

Dalilan da suka sanya naki gabatar da shaidar kammala karatu na na Sakandare -Muhammadu Buhari

Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Aljeriya, Walid Sadi, ya wallafa a shafinsa na X cewa, “Na hadu da kocin kasar Djamel Belmadi don tattauna abubuwan da ke tattare da wannan rashin nasarar, kuma mun cimma yarjejeniyar kawo karshen dangantakarmu da kuma dakatar da kwantiraginsa.”

Advertisement

Korar Belmadi ta zo ne a ranar da Ivory Coast mai masaukin baki ta kawar da kocinta Jean-Louis Gasset a tsakiyar gasar sannan Ghana ta kori Chris Hughton bayan ficewarta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending