Connect with us

News

Dubun Wani Gardi Ya Cika,An Kama Shi A Ɗakin Kwanan Ɗalibai A Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Jami’an Civil Defence’ reshen jihar Kano sun Yi nasarar damƙe wani gardi mai suna Muhammad Munzali ɗan garin Ƙaura Gidan Damo a ƙaramar hukumar Shanono.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar NSCDC, Ibrahim Abdullahi,shi ne ya tabbatar da kamen a yau Juma’a.

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Ya ce Jami’an sun damƙe wanda ake zargin ne da misalin karfe 10 na dare a ranar Laraba a lokacin da yake ƙoƙarin kutsawa cikin ɗakin kwanan ɗaliban na jami’ar Skyline wanda ke kan titin Sardauna Crescent, Nassarawa GRA,Kano

“Wanda ake zargin yayi ɓadda kama da shigar mata inda yayi ƙoƙarin kutsawa ɗakin kwanan ɗaliban,Ko Da aka cafke shi an same shi da layu a jikin sa,” cewar PRO .

A Cewar Ibrahim zuwa yanzu ana cigaba da gudanar da bincike domin gano hujjar sa na yin wannan kutse inda daga nan ne za a san wani mataki za a ɗauka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending