Connect with us

News

Mutane uku sun rasa ransu sakamakon rikicin kauraye a wurin gangi a Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

A ranar Lahadi ne wasu mutane uku suka rasa rayuwarsu a wani rikicin da ya barke tsakanin wasu ’yan daba a unguwar Darmanawa da ke Karamar Hukumar Tarauni a Jihar Kano.

Rikicin ya faru ne bayan wani magidanci mai shekara 59 ya shirya taron gangi domin murnar auren ’ya’yansa.

Atiku da Obi sun yi ganawar farko tun bayan shan kaye a zaɓen 2023

Daga nan ne ’yan daba suka yi amfani da wannan dama don gwada kwanji.

Daga bisani abin ya rikide zuwa kazamin fadan da ya yi ajalin mutum uku.

Advertisement

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kano, SP Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce an sanar da su cewa ana rigima a Darmanawa, sun aika jami’ansu inda daga bisani suka sami labarin cewa mutane uku sun rasa rayukansu.

SP Haruna ya bayar da tabbacin kama mutumin da ya shirya gangin da kuma wasu mutane biyu da ke anguwar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending