News
Wasu ‘yan bindiga sun harbe wani Mai POS
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wasu ‘yan bindiga da ke kan babura sun kashe wani mutum mai suna Mutiu Salako, POS a Oke Lantoro a Abeokuta jihar Ogun.
DAILY POST ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da karfe 6 na yammacin ranar Lahadi.
Yadda ‘Yan ta’adda 200 suka yi wa sojoji diran bazata a sanasanin Faskari
Wani sako da aka watsa ta WhatsApp da ke fadakar da jama’a game da lamarin ina aka danganta harin da kisan gilla mai alaka da kungiyar asiri.
Amma mai magana da yawun ‘yan sandan, Omolola Odutola, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin a matsayin wani lamari na yunkurin yin fashi da makami.
Odutola ya ce, ‘yan sanda a lokacin da suka kai samame yankin da aka aikata laifin, sun kama wasu mutane uku da ake zargi.
Wasu ‘yan bindiga biyu a kan babur sun harbe Mutiu Salako, ma’aikacin PoS wanda daga baya ya mutu a asibiti. Ba batun kisan ’yan kungiyar asiri ba ne, kamar yadda ake hasashe, amma an kama yunkurin kisan kai da wasu mutane uku da ake zargi bayan farmakin da ‘yan sanda suka kai yankin.”
