News
Shugaba Tinubu ya ba da umarnin sake duba kwamitocin gudanarwar manyan makarantu
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya ba da umarnin sake duba kwamitocin hukumar gudanarwar manyan makarantu da aka sanar kwanan nan a Najeriya kafin kaddamar da ja da baya da ake shirin yi wa wadanda aka nada.
Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwar da Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga a ranar Alhamis ne ya sanar da hakan a wata sanarwa mai taken ‘Shugaba Tinubu ya ba da umarnin sake duba kwamitocin gudanarwa na manyan makarantu.’
DA DUMI-DUMI: Gwamnan Kano Ya Sanar Da Dawowar Muhammadu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Kano.
Onanuga ya ce nadin “ba su nuna halin tarayya na kasar nan ba saboda wasu jihohi sun samu mutum daya kacal, yayin da wasu kuma suka samu da yawa.”
Tinubu ya amince da nadin akalla mutane 555 da za su yi aiki a matsayin Pro-Chancellor/Chairmen da membobin kwamitin gudanarwa na jami’o’in gwamnatin tarayya 111, polytechnics da kwalejojin ilimi.
To sai dai kuma bayan da jama’a suka yi ta cece-kuce, ciki har da kungiyar malaman jami’o’i reshen jihar Bauchi, wadda ta yi kira da a maido da wadanda aka rusa tun farko, shugaban ya ce a lokacin da ya ba da umarnin sake duba jerin sunayen ‘yan majalisar gwamnati, sun amince da hakan.
Za a gudanar da bikin rantsar da wadanda aka zaba a ranar 31 ga watan Mayu, 2024.
A cikin jerin sunayen akwai tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa Farfesa Attahiru Jega, wanda kuma aka nada shi a matsayin Pro-Chancellor kuma Shugaban Hukumar Gudanarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato ta Jihar Sakkwato. Mambobin sun hada da Mary Yisa, R. O. Kazeem da Farfesa Usman Musa da Dr. Anthony Usoro.
Kazalika akwai Wole Olanipekun, SAN, an nada shi Pro-chancellor kuma shugaban hukumar gudanarwa na jami’ar Legas, Akoka na jihar Legas.
Mambobin sun hada da Farfesa S. E. Ogbeide da Rufai Chanchangi da Misis Glory Ekpo-Oho, da kuma Patricia Yakubu, da dai sauransu.
