Connect with us

News

Joe Biden Ya Janye Daga Takarar Shugaban Amurka 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya janye ƙudirinsa na shiga zaɓen shugaban ƙasar da za a yi a watan Nuwamba.

Advertisement

Wannan na ɗauke ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

Zanga-Zanga : Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

Biden, ya ce yana da muradin neman sake tsayawa takara shugaban ƙasar, amma ya ce ya ɗauki matakin ne don kare muradin jam’iyyarsa da kuma ƙasarsa.

Advertisement

Biden ya ci gaba da fuskantar sabon matsin lamba kan haƙura da takararsa, bayan gwaji ya tabbatar yana ɗauke da cutar COVID-19.

A ranar Laraba ne fadar gwamnatin ƙasar ta fitar da sanarwar cewa shugaban mai shekara 81, ya nuna alamun cutar.

Advertisement

Sakatariyar yaɗa labaran shugaban, Karine Jean-Pierre, ta ce an yi wa shugaban rigakafi kuma yana samun sauƙi.

Ta ce shugaban ya killace kansa a gidansa da ke Delaware yayin da zai ci gaba da gudanar da ayyukansa ofishinsa daga gida.

Advertisement

Likitan Joe Biden, Kevin O’Connor, ya ce shugaban na fama da matsalar numfashi da zubar majina da tari, amma ya ce tuni ya fara shan magani.

Daga baya shugaban ya gode wa jama’a kan fatan alheri da suke masa a shafinsa na X (Twitter).

Advertisement

Sau biyu dai a baya ana tabbatar da shugaban na kamuwa da cutar COVID-

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending