News
Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin APC Kan batun yin zanga zanga
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaba Bola Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC karkashin kungiyar gwamnonin Progressives Forum a fadar sa da ke Abuja.
Taron wanda aka fara da misalin karfe 1, ya biyo bayan kiraye-kirayen da ake yi na zanga-zangar adawa da matsalar tattalin arziki a fadin Nijeriya.
Ko da yake ba a san ajandar taron ba, amma ana iya danganta shi da zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a ranar 1 – 10 ga Agusta.
Zanga-zangar wacce aka shirya a karkashin taken ‘EndBadGovernance’ ta samu karbuwa sosai a shafukan sada zumunta duk da cewa wadanda suka shirya zanga-zangar ba a bayyana sunansu ba,kuma ba babu sunan wata kungiya da ta dauki nauyi a hukumance ba.
Wannan taron ya biyo bayan kammala taron kungiyar gwamnonin Nijeriya da aka yi a daren Larabar da ta gabata, kuma ya biyo bayan soke taron Majalisar Tattalin Arzikin kasa da aka shirya gudanarwa a yammacin ranar Alhamis dinnan.
Wadanda suka hallarci taron sun hada da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ministan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Wale Edun da Abubakar Bagudu.
