News
An samu jagoran zanga zangar matsin rayuwa a unguwar tudun Yola dake Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jagoran masu zanga-zanga a nan Kano a unguwar tudun yola Auwal Baban Jimaga ya ce zanga-zanga babu gudu babu ja da baya, har sai gwamnatin tarayya ta biya musu muradansu.
Kwamared Auwal ya ce komai ya lalace a kasar nan talaka na fama da matsaloli masu yawa wanda su shugabanni basu damu da halin da talakawa ke ciki ba.
Ta cikin tattaunawar da aka yi dashi Auwal ya ce kayan masarufi sunyi tsada abinci ya fi karfin talaka, talakawa na kwana ba bu cin yau bare na gobe wanda hakanne ke kara haifar da damuwa da Kuma cutar da rayukan su
Ya kara da cewa sanin kowa ne bangaren lafiya da ilimi da sauran bangarori babu wani cigaba sai ko ma baya.
Ya Kuma ce matukar Gwamnati naso su janye zanga-zangar da suka shirya to dole ne su cika wadannan abubuwa kamar haka.
Jaridar inda ranka ta rawaito A Ranar 1 ga watan Augusta ne za’a fara gudanar da zanga-zanga dan kyamatar yunwa a fadin kasar
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
