Connect with us

News

Isra’ila ta kashe shugaban Hamas Ismail Haniyeh

Published

on

DAGA YASOR SANI ABDULLAHI 

An kashe shugaban Hamas Ismail Haniyeh a Iran, a cewar wata sanarwa da ƙungiyar da kuma jami’an gwamnatin Iran suka fitar.

Advertisement

Hamas ta ce Isra’ila ce ta kashe shugabanta ranar Laraba da sanyin safiya a samamen da ta kai a gidansa da ke Tehran.

Kano: Jagoran Zanga-Zanga Ya Bayyana Bukatar Su

A wata sanarwa da ta fitar, ƙungiyar ta bayyana juyayin rasuwar Haniyeh, mai shekara 62, wanda “miyagu masu tsananin kishin kafa ƙasar Isra’ila” suka kashe a gidansa da ke Tehran.

Advertisement

Haniyeh, wanda fitacce ne a fafutukar kare haƙƙin Falasɗinawam ya daɗe yana gwagwarmaya kan kisan ƙare-dangin da Isra’ila take yi a Gaza.

Gwamnatin Iran ta ce ta ƙaddamar da bincike kan kisansa, wanda take sa ran fitar da sakamakonsa nan ba da jimawa ba.

Advertisement

“An kai hari a gidan shugaban ɓangaren siyasa na Hamas, Ismail Haniyeh a Tehran, kuma sakamakon hakan shi da ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa sun yi shahada,” in ji wata sanarwa da shafin intanet na Sepah, mallakin rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps ya wallafa.

Kawo yanzu babu wanda ya ɗauki alhakin kisan, sai dai ana zargin Isra’ila da aikata shi, domin kuwa ta daɗe da shan alwashin kashe Haniyeh da sauran shugabannin ƙungiyar Hamas.

Advertisement

 

 

Advertisement

TRT Afirika 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending