News
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Janye Harajin VAT Kan Magunguna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta kammala aiki a kan dokar ofishin shugaban kasa ta janye harajin sayen kaya (VAT) a kan magunguna da na’urorin kiwon lafiya.
Da yake bayyana hakan a cikin wata sanarwa, mai magana da yawun ma’aikatar lafiya da walwalar jama’a, Alaba Balogun, yace an kammala aikin daidaita yadda za’a aiwatar da dokar yanzu saura a wallafata.
An Daure Direba Shekara 15 A Gidan Yari Bisa Samunsa Da Laifin Kashe Jami’in KAROTA
“Gaba mafi mahimmanci a dokar ita ce tabbatar da cewa hukumar tattara haraji ta Najeriya (FIRS) da takwararta ta yaki da fasa kwabri na iya fara aiwatar da shirin daina cazar harajin VAT a kan magunguna da na’urorin kiwon lafiya,” a cewarsa.
A cewar sanarwar, wallafa dokar da aka hade hancin bangarorinta na nufin cimma daya daga cikin manufofin ma’aikatar, na sakarwa harkar kiwon lafiya mara.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
