Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Amincewa Dillalan Man Fetur Sun Fara Dauko Man Fetur Kai Tsaye Daga Matatar Dangote angote

Published

on

Matatar Man Dangote ta zargi hukumar NUPRC da gazawa wurin gudanar da ayyukanta

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Gwamnatin tarayya ta bai wa ‘yan kasuwar man fetur izinin fara dauko mai kai tsaye daga matatar dangote ba tare da bin ta hannun Kamfanin Man Fetur na kasa, NNPCL ba.

Advertisement

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ministan kudi kuma shugaban kwamitin aiwatar da siyar da danyen mai ta hanyar amfani da kudin Naira, Wale Edun ya sanyawa hannu, domin karin haske kan yadda aka fara sayan danyen mai da kuma sayar da kayayyaki da kudin Naira.

A Daina Tunanin Gwamnatin Shugaba Tinubu Za Ta Sake Manufofinta —Jam’iyyar APC

Kwamitin da Edun ke jagoranta ya gudanar da taron masu ruwa da tsaki na biyu bayan fara aiki a ranar 10 ga watan Oktoba, domin tantance irin ci gaban da aka samu a shirin sayar da danyen mai da tataccen mai da kudin na Naira.

Advertisement

Sanarwar ta ce “masu kasuwancin albarkatun man fetur yanzu suna iya siyan man kai tsaye daga matatun mai na cikin gida ba tare da bi ta hannun kamfanin NNPC ba. ‘muna karfafa gwiwar dillalan man da su yi sayayya kai tsaye daga matatun mai bisa sharudan kasuwanci da aka kulla, wanda zai inganta kasar da kuma kasuwanci,”

Edun ya kuma ci alwashin cewa, nan da wani dan lokaci, matakan da aka dauka za su samar da ingantaccen yanayin kasuwanci don amfanin dukkan ‘yan Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending