News
Babban Hafsan Sojoji Janar Lagbaja Na Nan Da Ransa – Rundunar Sojin Najeriya
DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Rundunar sojin Najeriya ta yi watsi da rade-radin mutuwar babban hafsan sojin kasa (COAS), Taoreed Lagbaja, da wasu mutane suka yi a dandalin sada zumunta.
Sojojin sun karyata jita-jitar a wani sako da suka wallafa a shafinta na X ranar Lahadi, inda suka yiwa wani rubutun Jackson Ude lakabi da “Labarin Karya”.
TIRKASHI: Wani Mahaifi Ya Dana Wa ’Yarsa Budurwa Kyamarar CCTV A Kai Don Sa Mata Ido
Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya rawaito cewa wasu rahotanni na yanar gizo sun yi hasashen cewa Lagbaja, Laftanar Janar, ya rasu ne a wani asibiti da ba a bayyana ba a kasar waje.
Dukkanin rahotannin sun ambato Jackson Ude a matsayin majiyarsu ba tare da wani tabbaci a hukumance daga hedkwatar sojoji da tsaro ba.
Sai dai Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Onyema Nwachukwu, a ranar Asabar, ya ba da sanarwar cewa COAS na hutu tare da kula da lafiyarsa a wajen kasar.
Bayan haka Nwachuku ya ce ba abar wannan ofis babu kowa ba, Manjo Janar, Abdussalam Ibrahim, na rike da ofishin kafin Lagbaja ya dawo daga hutu.
” Komai da ake yi a aikin soja a tsare yake. Ba za a bar wannan sakatete ba babu wani da zai zauna a madadin babbana hafsan sojojin kasan ba.
Ya yi kira da mutane da su yi watsi da wannan jita-jita, yana mai cewa Lagbaja na nan a kuma ana sa ran dawowarsa idan ya kammala hutun sa da duba lafiyarsa.
