News
Hukumar NJC Ta Dakatar Da Alkalan Manyan Kotuna A Jahohi 2
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Majalisar kula da harkokin shari’a ta Najeriya (NJC) ta dakatar da Mai Shari’a G.C Aguma na babbar kotun jihar Ribas da Mai Shari’a A.O Nwabunike na babbar kotun jihar Anambra daga gudanar da harkokin shari’a.
An dakatar da alkalan 2 ne tsawon shekara guda ba tare da albashi ba sannan za’a cigaba da sanya idanu a kansu tsawon shekaru 2 a nan gaba.
Za’ A Dauki Tsawan Lokaci Kafin A Gama Gyaran Matsalar Wutar Lantarki A Arewacin Najeriya – Rahoto
A cewar sanarwar da NJC din ta fitar a yau Juma’a, an dauki wannan mataki ne yayin karo na 107 na taron majalisar da babban jojin Najeriya, Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta jagoranta tsakanin ranakun 13 da 14 ga watan Nuwambar da muke ciki.
Jumlar alkalai 5 aka hukunta saboda aikata laifuffuka daban-daban.
Muryar Amurka ta ruwaito cewa majalisar ta bada shawarar yiwa wasu alkalan 2 ritayar dole saboda shigar da bayanan karya game da shekarunsu na haihuwa.
An bada shawarar yiwa alkalan 2 da suka hada alkalin alkalan jihar Imo, Mai Shari’a T.E Chukwuemeka Chikeka da girandi kadin jihar Yobe, Kadi Babagana Mahdi, ritayar dole saboda samunsu da yin karya game da shekarunsu.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
