Politics
Shugaban Jam’iyyar APC Na Karamar Hukuma GezAwa Ya Gwangwaje Daliban Da Sukayi Saukar Alqur’ani Da Kyaututtuka
DAGA ALIYU DANBALA GWARZO.
Alhaji Sani yamadi Shugaban jamiyyar APC na karamar Hukumar Gezawa, ya gabatar da bada tallafin a yayin Taron saukar karatun Al Quran magirma a makarantar Tarbiyyatul Aulad dake jannarya a karamar hukumar Gezawa
Shugaban jamiyyar yace yabada Atamfofin Tare da kudin dinki naira Dubu Dari domin kara zaburar da daliban wajen cigaba da kokarin zuwa makaranta domin samun ilimin Addini, kuma hakan zaisa sauran dalibai na baya sukara zage dantse wajen cigaba da zuwa makaranta.
yakara da cewa “hakika irin wadannan Dalibai yadace ake kokarin taimakawa duba da yadda suka maida hankali wajen zuwa makaranta har Allah yabasu damar sauke Al Qurani mai girma, dan haka babu tukuicin da yakamata ayiwa Daliban sai da irin wanan tagomashi kuma ashirye muke mucigaba da tallafawa makaratun islamiyyu da dalibai a Gezawa baki daya.
Kazalika yamadi yayi kira ga matasa dasu maida hankali wajen neman ilimin Addini domin shine zai taimake su a duniya da lahira.
Daga karshe yayiwa wadannan dalibai fatan Alkairi tare da Fatan zasuyi amfani da abinda suka karanta domin samarwa da kansu gobe mai kyau.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
