Connect with us

News

Kano State Polytechnic Sun Tsunduma Yajin Aiki

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Ƙungiyar Malaman Kwalejin Fasaha reshen Jihar Kano, ta shiga yajin aikin gargadi na mako biyu da zai fara daga ranar 2 ga Disamba, 2024.

Advertisement

Wannan mataki an bayyana shi ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na kungiyar, Babangida Sa’adu, ya sanya hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.

Majalisar Wakilai Ta Dage Yin Muhawara Kan Dokar Haraji Har Sai Baba Ta Gani

An yanke shawarar shiga wannan yajin aikin ne a taron NEC na 112 na ASUP da aka gudanar a Abuja ranar 28 ga Nuwamba, 2024.

Advertisement

A lokacin wannan yajin aiki, dukkanin harkokin karatu a Polytechnic ta Jihar Kano za su tsaya cik.

ASUP ta taba bai wa gwamnatin tarayya da sauran hukumomin da abin ya shafa wa’adin kwana 15 don sake duba da janye manufofin da suka saba wa dokar Polytechnics da sauran dokokin gudanarwa a wannan bangaren.

Advertisement

Kungiyar ta zargi Gwamnati da rashin da’a da kuma raina wasu muhimman dokokin da suka kafa manyan makarantu mallakin jihohi da sauran kayan aikin gudanarwa.

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending