Connect with us

News

Ma’aikata A Kaduna Sun Fara Yajin Aiki Saboda Rashin Aiwatar Da Sabon Mafi Ƙarancin Albashi 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Ma’aikata a Jihar Kaduna, sun fara yajin aiki na mako guda saboda rashin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi a jihar.

Advertisement

Ƙungiyoyin Ƙwadago na NLC da TUC ne suka bayar da umarnin fara yajin aiki a ranar Litinin.

Shugaban Jam’iyyar APC Na Karamar Hukuma GezAwa Ya Gwangwaje Daliban Da Sukayi Saukar Alqur’ani Da Kyaututtuka

Shugaban NLC na jihar, Ayuba Suleiman, ya shaida cewar, gwamnatin jihar ta aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashin, amma ta kasa daidaita albashin sauran ma’aikatan jihar.

Advertisement

Sai dai gwamnatin jihar ta musanta hakan, inda ta bayyana cewa ta fara biyan ma’aikatan jihar Naira 72,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi a watan Nuwamba.

Mai Magana da Yawun Gwamnan jihar, Malam Ibraheem Musa, ya ce ƙarin albashi ba zai yiwu ba saboda ƙaracin kuɗaɗen shiga da jihar ke fama da shu.

Advertisement

Ya ce mafi yawan kuɗin da jihar ke kashewa na tafiya ne wajen biyan albashi da kuma biyan bashi.

Musa, ya bayyana cewa kashe ƙarin kuɗaɗe a kan albashi ba zai bar gwamnatin ta yi wa al’umma aiki ba.

Advertisement

Ya roƙi ma’aikatan jihar da su jira zuwa lokacin da abubuwa za su daidaita kafin yi musu sabon ƙari a albashinsu.

Har ila yau, ya ce gwamnatin ta bayar da motoci kyauta ga ma’aikata don sauƙaƙa musu zuwa wajen aiki.

Advertisement

Sai dai shugabannin ƙwadago sun dage cewa sai gwamnatin ta biya buƙatunsu, lamarin da bai kai su ga cimma matsaya ba.

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending