News
SABBIN KWAMISHINONI: Ba Za Mu Lamunci Shashanci A Gwamnatinmu Ba – Gwamna Kano
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Gwaman jihar kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana ƙudurin shi na ɗaukar matakin daya kamata ga dukkan kwamishinan daya kawo masu wasa a cikin aikin gwamnatin su.
Gwaman Kano ya bayyana haka ne a yayin zaman majalisar zartarwa karo na 23 da ake gudanarwa a gidan Gwamnatin jihar.
Nan Ba Da Jimawa Za A Ƙara Kuɗin Kiran Waya Da Data — Gwamnatin Tarayya
”Yanzu, kuma a wannan lokaci da muke ciki ba zamu lamunci dukkan wani shashanci ba, dan haka dukkan kwamishinan da ya kawo mana wargi ko wasa zamu ɗauki matakin da ya kamata akan shi.
Zamu yi amfani da wannan dama dan ƙara jan hankalin ku sababbin kwamishinoni da ku tsaya ku haɗa kan ku waɗanda kuka samu dan aiki tare da zai ɗaga martabar Jihar Kano.”
Advertisements
