News
Kananan Hukumomi Za Su Karbi Kason Kudinsu Kai Tsaye Daga Gwamnatin Tarayya A Watan Janairu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Fadar shugaban kasa ta sanar da cewa daga karshen watan Janairu, kananan hukumomi a fadin Najeriya za su fara karbar kason kudadensu kai tsaye daga kwamitin asusun bai daya na gwamnatin tarayya (FAAC), wanda ke nuna wani gagarumin mataki na cin gashin kan kananan hukumomi.
Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa Sunday Dare ne ya bayyana hakan a wata hira da yayi da gidan talabijin na Arise News a daren ranar Alhamis.
Ya nanata kudurin Shugaba Bola Tinubu na aiwatar da hukuncin Kotun Koli na Yuli 2024, wanda ya ayyana ikon da jihohi kan kudaden kananan hukumomi ya sabawa tsarin mulki.
-
News7 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
