Connect with us

News

Kananan Hukumomi Za Su Karbi Kason Kudinsu Kai Tsaye Daga Gwamnatin Tarayya A Watan Janairu

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Fadar shugaban kasa ta sanar da cewa daga karshen watan Janairu, kananan hukumomi a fadin Najeriya za su fara karbar kason kudadensu kai tsaye daga kwamitin asusun bai daya na gwamnatin tarayya (FAAC), wanda ke nuna wani gagarumin mataki na cin gashin kan kananan hukumomi.

Advertisement

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa Sunday Dare ne ya bayyana hakan a wata hira da yayi da gidan talabijin na Arise News a daren ranar Alhamis.

Jami’an Hukumar Hisbah Sun Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Ya nanata kudurin Shugaba Bola Tinubu na aiwatar da hukuncin Kotun Koli na Yuli 2024, wanda ya ayyana ikon da jihohi kan kudaden kananan hukumomi ya sabawa tsarin mulki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending