News
An Kone Adaidaita Sahun Barayin Waya a Kano
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wasu fusatattun matasa sun kona wata Adaidaita Sahun, da ake kyautata zaton na masu satar waya ne akan titin Ibrahim Taiwo dake birnin Kano.
Bayan kone baburin an kuma yi nasarar kama masu babur din tare da mika su hannun jami’an tsaro.
Mutane Saba’in Da Bakwai Sun Rasa Rayukansu A Ya Yin Fashewar Tankar Mai A Neja
Kakakin Rundunar ‘Yan sandan Jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin, sannan ya ce wadanda ake zargin suna hannun jami’an tsaro.
Kiyawa, yace an samu waya guda biyar a wajen su.
Jaridar INDA RANKA ta ruwaito cewa Lamarin dai ya faru a daren yau asabar.
Satar waya a wajen wasu daga cikin masu Adaidaita Sahun ta zama ruwan dare a wasu sannan jihar Kano.
wanda irin haka ta faru kwanakin baya a kofar shiga asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano, da aka samu wasu masu sace waya a babur inda aka kone musu babur din suma.
