Connect with us

News

Marken Mahuta: Kauyen Da Kalubalen Ilimi Da Rashin Lafiya Suka Addaba A Kano 

Published

on

FB IMG 1739126311881 (1)

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Marken Mahuta, wani ƙauye a karamar hukumar Ɗambatta, jihar Kano, yana cikin mawuyacin hali sakamakon rashin asibiti da makarantu masu inganci.

Advertisement

Tun shekaru aru-aru, al’ummar ƙauyen suna rayuwa ba tare da cibiyar lafiya ko makarantar da ke iya samar da nagartaccen ilimi ba. Wannan ya haddasa mace-macen mata masu juna biyu, yawaitar jahilci, da rashin kyakkyawar makoma ga matasa.

JAMB Ta Gargadi Cibiyoyin Da Ke Yi Wa Dalibai Rajistar Jarabawa Da Dare Da Su Daina Haka

Kalubalen Ilimi a Marken Mahuta

Advertisement

Rahoton KANO TIMES ya nuna cewa akwai wahala a neman ilimi a wannan ƙauye, musamman ga ‘yan mata.

“Babu wata yarinya da ta taɓa kammala firamare,” in ji Malam Bala, mazaunin ƙauyen. Maza kuma na fama da matsalolin rashin kayan aiki, kwararrun malamai, da wasu ƙalubalen al’adu.

Advertisement

Wata mahaifiya, Hajiya Sa’adatu, ta bayyana damuwarta:

> “Na yi mafarkin ganin ‘yata ta zama malama, amma wannan mafarki yana neman wargajewa. Babu malama mace a wannan ƙauye.”

Advertisement

Lafiya: Mata da Yara na cikin Hatsari

Rahotanni sun bayyana cewa ana yawan samun mace-macen mata masu juna biyu a Kano, inda mata 377.8 a cikin duk haihuwa 100,000 ke mutuwa.

Advertisement

A Marken Mahuta, mata masu nakuda suna rasa jariransu ko rayuwarsu saboda babu asibiti a kusa.

> “Mata masu juna biyu su ne mafi shiga tsananin wahala. Suna rasa rayukansu kafin su isa wani asibiti a Ɗambatta,” in ji Hajiya Binta.

Advertisement

Wata uwa mai suna Yalwa ta ce:

> “Ba mu da asibiti a ƙauyenmu. Lokacin da na yi nakuda, na gamu da ciwo mai tsanani, amma babu likita da zai taimake ni. A ƙarshe, na rasa jaririna.”

Advertisement

Rashin Hanya da Magunguna Masu Inganci

Idan lokacin damina ya zagayo, ƙauyen Marken Mahuta na komawa tamkar akurki, saboda babu hanyar shiga ko fita daga garin.

Advertisement

Hakazalika, mazauna ƙauyen na rayuwa ne ba tare da samun magungunan zamani ba, sai dai su yi amfani da na gargajiya.

Malam Yusuf ya ce:

Advertisement

> “Mun dogara ne da magungunan gargajiya da kantunan magani masu zaman kansu. Mun rasa cibiyar lafiya tun bayan da ta kone shekaru da suka gabata.”

Barazanar Cututtuka Masu Yaduwa

Advertisement

Zazzabin cizon sauro na ɗaya daga cikin manyan matsalolin rashin lafiya da ke addabar ƙauyen. Haka kuma, yara da yawa na mutuwa a lokacin damina saboda kamuwa da cututtuka.

Malam Sani ya ce:

Advertisement

> “Za a iya warkar da yara idan da akwai likita ko cibiyar lafiya mai inganci.”

Rashin Cika Alkawura Daga Gwamnati

Advertisement

A duk lokacin da aka ce siyasa ta zo, ‘yan siyasa na dafifin zuwa ƙauyen, duk kuwa da matsalar rashin hanya.

Duk da tarin alkawuran da suka yi, ba a sake gina cibiyar lafiya ba tun bayan konewarta, kuma ba a gyara hanyoyi ba.

Advertisement

Malam Bala ya ce:

> “Ko da muka roƙi taimako daga gwamnati, ba mu samu mafita ba. Har yanzu, babu wani cigaba da muka samu a gwamnatance.”

Advertisement

Mazauna Marken Mahuta na Neman Taimako

Mazauna ƙauyen sun yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni su taimaka wajen samar da asibiti, gyaran hanyoyi, da tallafa wa ilimin yara mata.

Advertisement

> “Ba damuwarmu samun alatun duniya ba ne, mu fatanmu samun abubuwan more rayuwa kamar su ilimi, kiwon lafiya, da hanya mai kyau,” in ji Malama Amina.

Rashin Jin Ba’asi Daga Hukumomi

Advertisement

Kokarin jin ta bakin Kwamishinan Lafiya na Kano, Dr. Abubakar Yusuf Labaran, da Kwamishinan Ilimi, Dr. Ali Haruna Makoda, ya ci tura.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto,

Advertisement

ba a samu wata sanarwa daga gare su ba game da matsalolin ƙauyen Marken Mahuta.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending