Connect with us

News

Majalisar Dokokin Kano Ta Gayyaci Shugaban Karamar Hukuma Bisa Rushe-Rushe A Kasuwar Rano

Published

on

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce Babu Gudu Babu Ja Da Baya Kan Zaben Kananan Hukumomin Da Aka Shirya Yi

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta gayyaci shugaban karamar hukumar Rano domin bayani kan rushe-rushe da aka gudanar a kasuwar Rano, lamarin da ya haifar da cece-kuce a tsakanin ‘yan kasuwa da al’umma.

Advertisement

Dan-majalisa mai wakiltar karamar hukumar Rano, Alhaji Ibrahim Muhammad Rano, ne ya gabatar da kudiri na gaggawa a zaman majalisar na yau, inda ya bukaci a kai dauki ga ‘yan kasuwar da abun ya shafa.

Rashin Tsaro: Mutum 91,740 Suka Rasa Rayukasu A Najeriya Cikin Shekaru 13 – Rahoto

Alhaji Ibrahim Rano ya bayyana cewa, rushe-rushen da aka gudanar ba tare da wata sanarwa ba ya jefa daruruwan ‘yan kasuwa cikin halin kaka-ni-kayi, wanda hakan ke barazana ga tattalin arzikin yankin.

Advertisement

Majalisar ta amince da kudirin, tare da bukatar shugaban karamar hukumar ya bayyana gaban ta domin karin bayani kan dalilan da suka sa aka gudanar da rushe-rushen ba tare da la’akari da halin da al’umma ke ciki ba.

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar da abin ya shafa sun bukaci gwamnatin jihar ta shiga tsakani domin tallafa musu, tare da neman a dakatar da rushe-rushen nan gaba.

Advertisement

Majalisar ta bayyana cewa, za ta ci gaba da bibiyar lamarin don tabbatar da adalci da kare hakkokin al’umma.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending