News
Ana Zargin Jami’an SUBEB 6 Da Karkatar Da Naira Miliyan 96
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta (EFCC) reshen Ilorin ta gurfanar da wasu jami’an Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar Kwara (SUBEB) a gaban kotu. Ana tuhumar waɗannan jami’an da aikata laifuka huɗu na cin amana da karkatar da kuɗaɗen gwamnati, wanda ake cewa sun kai naira miliyan 96.
A cewar sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na EFCC, Dele Oyewale ya fitar, jami’an da ake tuhuma sun haɗa da:
Ahmed Husain Olarewaju – Daraktan Kuɗi da Kayayyaki
Omole Omololu John – Mai Kula da Lissafin Kuɗi
Fatai Oyerinde – Ko’odinatan Sashen Albashi
Mujeeb Ibrahim – Jami’in Lissafi
Salami Temitope Bashir da Dauda Aweda Quozim – Ma’aikatan Sashen Albashi
Ana zargin cewa tsakanin shekarar 2018 zuwa 2020, waɗannan jami’an (SUBEB) sun haɗa baki wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnatin jihar zuwa aljihunsu, inda suka raba a tsakaninsu.
Bayan karanta tuhumar, dukkan wadanda ake tuhuma sun musanta aikata laifin. Lauyan EFCC, Andrew Akoja, ya nemi a sanya ranar fara shari’a tare da tsare su a gidan gyaran hali, yayin da lauyansu, Abdullahi Lawal, ya nemi a ba su beli.
Alƙalin kotu, Mai Shari’a Akanbi, ya ɗage shari’ar zuwa ranar Laraba, 16 ga Afrilu, 2025 domin ci gaba da sauraron ƙarar, kuma ya bada umarnin a tsare waɗanda ake tuhuma a gidan gyaran hali na Ilorin har zuwa lokacin shari’a.
Wannan lamari na ƙara jaddada muhimmancin yaki da cin hanci da rashawa, musamman a fannonin ilimi inda kuɗaɗen gwamnati ke taka muhimmiyar rawa wajen inganta tsarin ilimi a jihohi.
