News
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Bukatar Kafa Sabbin Jami’o’i 200
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta yi watsi da bukatar majalisun dokokin tarayya na kafa sabbin jami’o’i guda 200, tana mai cewa abin da ya fi dacewa shi ne inganta jami’o’in da ake da su a halin yanzu.
Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da ministoci ke shiryawa, wanda aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja. Ya ce Najeriya na da jami’o’i 278, inda 64 ke karkashin Gwamnatin Tarayya, 67 na jihohi, yayin da 147 ke zaman kansu.
Ba Sauya Jam’iyya Ke Da Muhimmanci Ba, Sai Sauya Gurbataccen Tunani Don Ceto Arewacin Najeriya
A cewarsa, jami’o’in masu zaman kansu na iya daukar dalibai 875,000 kacal, wanda ke wakiltar kaso 7.5% na jimillar daliban jami’o’in kasar. Ministan ya kara da cewa, “Yanzu abin da ke gaban gwamnati ba kirkirar sabbin jami’o’i ba ne, sai dai kula da ingancin wadanda ake da su.”
Wannan mataki na gwamnati ya janyo cece-kuce daga wasu ‘yan Najeriya da ke ganin bukatar kara yawan jami’o’i don rage cunkoso da samar da karin guraben karatu ga matasa.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
