Connect with us

News

NAPTIP ta tseratar da yara 35 da za ai safarar su zuwa nahiyar turai

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar Yaƙi da Safarar Ɗan’adam, NAPTIP ta tseratar da yara 35 da za a yi safarar su zuwa nahiyar Turai a Ƙasar Nijar.

Shugaban Shiyyar Kano na hukumar, Abdullahi Babale shi ne ya baiyana haka a wata tattaunawa da Kamfanin Daillancin Labarai na Ƙasa, NAN a jiya Juma’a.

Advertisement

Ya ce an miƙa waɗanda a ka tseratar ɗin ga jami’an Hukumar kula da Shige da Fice ta Ƙasa, inda su kuma su ka miƙa su ga Hukumar NAPTIP a bodar Kongolam da ke Maiadua a Jihar Katsina.

Ya ce waɗanda a ka tseratar ɗin sun haɗa da maza 6 da mata 29 kuma ƴan shekaru 6 ne zuwa 42 da a ka yi safarar su da ga jihohin Ondo, Lagos, Enugu, Anambra, Oyo, Imo, Ogun, Ekiti, Edo, Osun, Kogi da Abia.

Advertisement

“Za a tafi da su zuwa nahiyar Turai ne ta bodar Nijar kuma mun fara bincike a kan lamarin,” in ji Babale

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending