News
Babban Taro: APC ta fara sayar da fom ɗin ƴan takara kuma N20m ne na takarar shugabancin jam’iya
Daga maryam Bashir musa
Jam’iya mai mulki ta APC ta fara sayar da fama-faman ƴan takarar shugabancin jam’iya a babban taron da za a ta yi ranar 26 ga watan Maris.
Shugaban Matasa na Ƙasa na riƙon ƙwarya, Ismail Ahmed ne ya baiyana hakan ga manema labarai a Abuja a jiya Talata bayan fitowa da ga wata ganawar sirri.
Ahmed ya ce kwamitin ne ya ɗora masa alhakin sanar da fara sayar da fama-faman na dukkanin gurabe, har da ma na shiyya-shiyya da kuma na ƙasa baki ɗaya.
Ya ce kwamitin ƙoli na jam’iyar ta amince da sayar da fom ɗin shugaban jam’iya na ƙasa kan Naira miliyan 20, sai kuma na sakataren jamiya na ƙasa da na Mataimakin Shugaban Jam’iya na Ƙasa, shiyyar kudu da arewa da za a sayar da shi kan Naira miliyan 10.
Ahmed ya ƙara da cewa fim ɗin duk wani gurbi a kwamitin ƙoli, za a sayar da shi Naira miliyan 5.
Sai kuma fim ɗin duk wani gurbi a kwamitin zartaswa na ƙasa, za a sayar da fom ɗin sa kan Naira miliyan 1.
Ya ce dukkanin wasu gurabe a bangaren shiyya, banda na Mataimakin Shugaban Jam’iya na Ƙasa, za a sayar da fom ɗin sa Naira dubu 500.
Ahmed ya ƙara da cewa za a sayar wa da mata da masu nakasa fom ɗin ko wanne gurbi kan kashi 50 na kuɗaɗen da a ka sanya.
-
News4 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
-
News2 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ayyana 1 Ga Satumba A Matsayin Ranar Hutun Bikin Takutaha
