News
An Kashe Sama Da Mutane 1,700 A Rikicin Iyakoki Da Muhalli A Najeriya — RAHOTO
Akalla mutane 1,796 ne suka rasa rayukansu sakamakon rikicin iyaka da na al’umma a sassa daban-daban na Najeriya daga Janairu 2018 zuwa Agusta 2025.
Wannan na cikin bayanan da wata ƙungiya mai zaman kanta, Foundation for Partnership Initiatives in the Niger Delta (PIND), ta fitar, wadda ke bibiyar rikice-rikice musamman a yankin Neja Delta.
SERAP Da Wasu Ƙungiyoyi 55 Sun Nemi Akpabio Ya Sauka Daga Kujerar Shugaban Majalisar Dattawa
Rahoton ya nuna cewa daga shekarar 2018 zuwa 2022, mutum 676 ne suka mutu a irin wadannan rikice-rikice, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Amma daga 2023 zuwa 2025, yawan mace-macen ya karu matuƙa, musamman a yankunan Kudu da Arewa ta Tsakiya.
A jihar Cross River kaɗai, an samu sama da mace-mace 400 tsakanin Janairu 2020 da Disamba 2023 sakamakon rikicin ƙasa.
Haka zalika, fiye da mutum 650 ne suka mutu a jihohin Delta da Bayelsa sakamakon rikicin iyaka da ƙasa.
PIND ta ce rikicin Okuama da ya auku a jihar Delta da kuma na Igbomotoru a Bayelsa, wanda ya haɗa da jami’an tsaro, na iya ci gaba idan ba a ɗauki mataki ba.
Haka nan kuma rahoton ya lissafa wasu manyan hare-hare da suka hada da kisan mutane 14 a Agbudu da ke Kogi, da kuma rikicin fili a jihohin Benue da Enugu.
Masana tsaro sun ce gazawar aiwatar da Dokar Amfani da Ƙasa (Land Use Act) da kuma rashin fayyace iyakokin ƙasa ne ke haddasa yawaitar wadannan rikice-rikicen.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
