News
A NAJERIYA BA SHUWAGABANNI AKE DA SU BA, CLUB ƊIN ƁARAYI NE KE MULKI – Cewar Sheikh Zakzaky
Advertisements

Daga mujahid danllami garba
Daga Cikin Jawaban Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya Sheikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana cewa “Su Al’umma Suna Sa Ran Macucinsu Ne Ya Zama Macucinsu, wannan kuwa abu ne da ba Zai Taɓa Yiwuwa Ba, Ba Yadda Za’ayi Macucinka Ya Zamo Macecinka
Lallai Ba Abu Ne Mai Yuwuwa ba Lalatacce Ya Kawo Gyara, Gyararre Ne Yake Kawo Gyara.”
Da aka Tambayesa Dan gane da Shugabannin Siyasa a Najeriya Ya bayyana cewa, a Najeriya ba Shugabanni Ake dasu ba Club ne na Ɓarayi da Suke Wawushe Dukiyar Al’ummar Suke Mulki”
Malamin Ya ci Gaba da Cewa” Waɗannan Lalatattun Ƴan Siyasan Ba Za Su Taɓa Fitar Da Mutane Daga Ƙangin Da Suke Ciki Ba, Don Su Suke Jefa Su (Acikin Ƙangin)!… Inji Shaikh Zakzaky.
Advertisements
