Connect with us

News

Kungiyar VOGPA Ta Bukaci A Dakatar Da Shagulgulan Kauyawa A Kano 

Published

on

1747142888819

Kungiyar Muryar Jama’ar Karamar Hukumar Gwale, wato Voice of Gwale LG People’s Association (VOGPA), ta yi kira ga hukumomin tsaro da na al’adu da su dakatar da sabon salo na shagulgulan da ya fara yaduwa a yankin, wanda kungiyar ta bayyana a matsayin barazana ga tarbiyyar ’yan mata.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakatarenta, Comrade Waleeth Adam Bako, ya fitar a ranar Talata, inda ta ce ana gudanar da wani biki da ake kira “Kauyawa” wanda ke gudana da dare, kuma cike da abubuwan da ke sanya ’yan mata fadawa halayen da ba su dace ba.

Advertisement

’Yar Shekara 19 Ta Kashe Kanta Bayan Samun Maki 190 A JAMB

“Kowa ya sani cewa shagulgulan Kauyawa suna kara jefa ’ya’yanmu mata cikin duhun rayuwa. Wannan abu na iya lalata duk tarbiyyar da iyaye ke kokarin ba su,” in ji sanarwar.

Kungiyar ta bukaci shugaban karamar hukumar Gwale, Hon. Abubakar Mu’azu Mojo, da ya dauki mataki cikin gaggawa domin kare al’adun yankin da kuma ceton matasa daga fadawa tarkon miyagun dabi’u.

Advertisement

A karshe, kungiyar ta roki ubangaji ya ba jihar Kano zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending