Politics
Akwai Yiwuwar Kwankwaso Ya Zama Abokin Takarar Tinubu A 2027
Rahotanni da ga Jaridar BUSINESS DAY na nuni da cewa Shugaba Bola Tinubu na iya sauya mataimakinsa Kashim Shettima da Sanata Rabi’u Kwankwaso a 2027.
Majiyoyi daga Abuja sun bayyana cewa hakan ne yasa Abdullahi Ganduje bai marawa Shettima baya ba a taron jam’iyya da aka yi a Gombe.
Iran ta yi wa sansanonin sojojin Amurka da ke Qatar da Iraqi luguden makamai masu linzami
Wata majiya daga APC ta ce Kwankwaso yana samun goyon bayan jiga-jigan jam’iyyar domin ƙarfafa damar zarcewar Tinubu a zaɓen 2027.
Majiyar ta ce an fara tattaunawa da Kwankwaso, kuma ya kai ziyara ga Shugaban ƙasar domin samun goyon bayansa cikin ƙanƙanin lokaci.
Kwankwaso na da tasiri sosai a Arewa ta hanyar ƙungiyar Kwankwasiyya, lamarin da ke jan hankalin shugaban ƙasa Tinubu da jam’iyyar APC.
Tsohon Gwamnan Kano wanda yayi mulki sau biyu, Kwankwaso, shi ne jagoran jam’iyyar NNPP wacce ke mulkin jihar Kano a halin yanzu.
Ya taɓa riƙe muƙamin Ministan Tsaro a zamanin Obasanjo, kuma ya wakilci Kano ta Tsakiya a Majalisar Dattawa daga 2015 zuwa 2019.
Masu tsara siyasar Tinubu na duba yadda za su lashe zabe a Kano dake da ƙananan hukumomi 44 da masu kaɗa ƙuri’a sama da miliyan biyar.
