News
Lokacin Siyasa Maras Ma’ana Ya Wuce A Kano — Waiya
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce lokaci ya wuce da za a ci gaba da siyasar banza da bata da amfani ga al’umma.
Waiya ya bayyana haka ne a ranar Juma’a yayin rantsar da sabbin shugabannin ƙungiyar masu magana a kafafen yaɗa labarai, wato GAUTA Club, a jihar Kano.
Ba Za Mu Bawa Kwankwaso Tikitin Takarar Shugabancin Kasa A Jam’iyyarmu Ba —NNPP
Ya ce, “Tsarin shugabanci ba ya da alaƙa da bambancin jam’iyya. Abin da ya fi muhimmanci shi ne a samar da ci gaba da kuma tsaftace harkokin masu magana a kafafen yaɗa labarai ta yadda za su dace da zamani.”
Kwamishinan ya bayyana cewa siyasar da za ta amfani jama’a da mutunta ra’ayoyin juna ita ce siyasar da ake bukata a yanzu.
“Lokaci ya wuce na siyasar da ke haifar da rikici da rarrabuwar kawuna. Lokaci ne na yin siyasa da za ta ciyar da mutane gaba da amfani da dimokuraɗiyya wajen kyautata rayuwar al’umma,” in ji Waiya.
Ya shawarci masu magana a kafafen yada labarai da su rika kare mutuncin ra’ayinsu ba tare da cin zarafin wani ko ɓata masa suna ba.
Shugabannin GAUTA da aka rantsar su ne:
Alhaji Bashir Adamu Gaya
Hon. Idris Danzago
Alhaji Isa Bello Ja
Alhaji Ibrahim Dan Adamdam
Alhaji Damina Ali Gwarzo
Alhaji Auwalu Maiturare Bichi
Kwamared Rabiu Bala
Muhammad Idris
Hon. Danjummai Gwoska
Injiniya Muhammad Tarauni
Lawan Sofi Dammasanin Gaya
Hajiya Binta Sayyadi
Hajiya Habiba Dandalla
Hon. Aminu Bichi
Waiya ya ce gwamnati za ta ci gaba da goyon bayan duk wani yunkuri da zai
inganta aikin kafafen yada labarai a jihar.
