Connect with us

News

Jami’an NSCDC Sun Kama Wani Da Ake Zargi Da Dillancin Miyagun Kwayoyi A Kano

Published

on

NSCDC

Jami’an Hukumar  NSCDC a jihar Kano sun kama wasu maza biyu da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi da kuma fasa gidaje.

Mai magana da yawun rundunar NSCDC ta jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da kama mutanen, inda ya ce an cafke su ne a lokuta daban-daban bisa bayanan sirri da suka samu daga jama’a.

Advertisement

Shugaba Tinubu ya taya dalibai yan Najeriya uku da suka yi fice a Ingilishi da Muhawara da nuna basira a duniya murna

Abdullahi ya bayyana cewa an kama wani da ake kira Ahmed yayin da yake cikin aikata laifin sayar da kuma rarraba haramtattun ƙwayoyi a unguwarsu.

A wani samame daban, jami’an NSCDC sun kuma kama wani saurayi mai suna Muhammad Abbas, mai shekara 22, a unguwar Gurungawa da ke karamar hukumar Kumbotso. Ana zarginsa da fasa gidajen mutane tare da satar kayayyaki masu darajar dubban naira.

Advertisement

Abdullahi ya ce za a gurfanar da dukan waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike. Ya kuma yi kira ga jama’a da su cigaba da kasancewa masu lura da yanayi tare da bayar da bayanai masu amfani da za su taimaka wa hukumomin tsaro wajen yaƙi da aikata laifi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending