Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Bude Wa ‘Yan Zaman Makoki Wuta

Published

on

yan bindiga sun sace mutane

Rundunar ’yan sandan Jihar Anambra, ta fara bincike kan kisan wasu mutum huɗu da ’yan bindiga suka yi lokacin da suke zaman makoki.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun buɗe wa masu makokin wuta ne a ranar Alhamis a garin Ogidi, da ke Ƙaramar Hukumar Idemili.

Advertisement

Masu Zuwa Daurin Aure 19 Sun Rasu Bayan Rushewar Gada A  Zamfara

Harin ya yi sanadin mutuwar mutum huɗu tare da jikkata aƙalla mutum 15.

Kakakin rundunar, Tochukwu Ikenga, ya ce suna zargin harin ya shafi rikicin ƙungiyoyin asiri ne.

Advertisement

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro da suka isa wajen sun gano harsasai 16, kuma za su yi amfani da su wajen bincike.

Ikenga, ya ce nan gaba za su sanar da jama’a abin da binciken nasu ya gano.

Advertisement

 

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending