News
Babu Abin Da Za Mu Rasa Idan Nijeriya Ta Daina Hulɗa Da Amurka – Sheikh Gumi
Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan na Nijeriya Sheikh Ahmad Mahmud Gumi ya bayyana cewa babu abin da Nijeriya za ta ragu da shi idan ta daina hulɗa da Amurka.
Ya bayyana haka ne a cikin ɓangaren wata hira da TRT Afrika Hausa ta yi da shi a daidai lokacin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Nijeriya na ɗaukar matakin soji a kanta.
“Ba Amurka ce kaɗai ƙasa a duniya ba da har za ka rasa wani abu idan ka daina hulɗa da ita, idan kayan ƙere-ƙere ne akwai China, idan kayan ƙarfi ne [makamai] akwai Rasha,” in ji Sheikh Gumi.
“Akwai ƙasashe da suke rayuwa waɗanda ba su san akwai wani abu Amurka ba, wannan ƙasar ba ta nuna mana tana ƙaunarmu ba, sai dai ta tatse manmu, ta raba mu, ta cutar da mu,” kamar yadda ya ƙara da cewa.
Sheikh Gumi ya jaddada cewa Amurka ba ta neman Nijeriya da alkhairi inda ya yi zargin cewa Amurkar na cikin waɗanda suka rinƙa taimaka wa yankin Biafra da ke son ɓallewa daga Nijeriya a lokacin yaƙin basasa.
Fitaccen malamin ya bayyana cewa Musulmai da Kirista suna zaune lafiya, babu ƙamshin gaskiya a kalaman Trump na Musulmi na kashe Kiristoci a Nijeriya.
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News15 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
