News
Jigawa: ‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kona Mahaifinsa Har Lahira A Kazaure
Rundunar ’yan sanda a Jihar Jigawa ta kama wani matashi mai suna Kabiru Nuhu mai shekaru 27 bisa zargin hallaka mahaifinsa mai shekaru 60 ta hanyar kona shi da wuta a karamar hukumar Kazaure.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Shiisu Lawan Adam, ya fitar, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar 1 ga watan Afrilu a unguwar Lokon Malamai da ke kusa da rukunin gidaje na Magama a cikin garin Kazaure.
Dakarun Soji Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Sace Daga Cocin Kaduna
Ya ce rundunar ta samu rahoton faruwar lamarin da misalin karfe 6:30 na safe, inda nan take aka tura jami’ai zuwa wurin domin daukar matakin gaggawa. Jami’an sun garzaya da wanda abin ya shafa zuwa asibiti domin ceto rayuwarsa, sai dai likitoci sun tabbatar da rasuwarsa.
A cewar kakakin rundunar, binciken farko ya nuna cewa lamarin ya faru ne kimanin mintuna 30 kafin a kai rahoto, inda ake zargin matashin ya zuba wani abu mai saurin kamawa da wuta — wanda ake kyautata zaton man fetur ne — a jikin mahaifinsa kafin ya cinna masa wuta.
Bincike ya kai ga cafke wanda ake zargin, inda aka same shi da raunuka a goshinsa, hannaye da kuma yatsun kafa, lamarin da ke kara karfafa zargin hannu a cikin wannan aika-aika.
Rundunar ta ce a halin yanzu wanda ake zargin yana tsare, kuma za a mika shi zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar da ke Dutse domin zurfafa bincike tare da gurfanar da shi a gaban kotu.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Haruna Alaba Yahaya, ya yi Allah-wadai da wannan lamari, yana mai jaddada cewa rundunar ba za ta lamunci irin wannan aika-aika ba.
Haka kuma, ya bai wa al’ummar jihar tabbacin cewa za a tabbatar an yi adalci a kan lamarin.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
