Connect with us

News

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mutane 14 Bisa  Zargin Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Yobe

Published

on

1 2 1 1024x413

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta kama mutane 14 da ake zargi da safarar da kuma sayar da miyagun ƙwayoyi, bayan wani samame da jami’anta suka kai maboyar masu aikata laifuka a Ƙaramar Hukumar Jakusko.

Mai magana da yawun rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce samamen ya gudana ne a guraren da ake zargin ana harkokin miyagun ƙwayoyi a Kasuwar Buduwa da ke Jakusko.

Dakarun Soji Sun Hallaka ‘Yanta’adda’ Fiye Da 300 A Zamfara

Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne yayin da ake zargin suna sayarwa da kuma amfani da miyagun ƙwayoyi. Daga cikin waɗanda aka kama akwai Hamisu Umar (20), Usman Wakili (25), Aliyu Mohammed (20), Hassan Ali (35), Dudduwa Dorsha (27), Adamu Hussaini (27), Sale Adamu (27), Adamu Umaru (25), Babaru Hassan (28), Dangi Maikudi (22), Hassan Audu (29), Abubakar Usman (29), Ahmadu Waziri (23) da Daudu Yusuf (20).

A cewar rundunar, an kuma ƙwace sama da fakiti 300 na miyagun ƙwayoyi iri-iri, ciki har da Tramadol, ƙwayoyin Vega, tabar wiwi da sauran haramtattun ƙwayoyin da doka ta hana.

Sanarwar ta ƙara da cewa bincike kan lamarin na ci gaba, yayin da waɗanda ake zargin ke bai wa jami’an tsaro bayanan da za su taimaka wajen gano tare da cafke sauran waɗanda ake zargi da hannu a wannan haramtacciyar harka. Za a gurfanar da su a gaban kotu bayan an kammala bincike.

Advertisement

 

 

DAILY POST

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending