Connect with us

News

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mutane 5 Bisa Zargin Samar Da Jabun Magungunan Gargajiya A Kano 

Published

on

IMG 20260814 WA0003

Rundunar ƴan sandan shiyya ta ɗaya a Kano ta kama mutane biyar bisa zargin yin kwaikwayon wani likitan magungunan gargajiya da kuma samarwa, siyarwa da rarraba magungunan gargajiya na jabu da sunansa.

An kama waɗanda a ke zargin ne bayan rundunar ta karɓi ƙorafi daga Dakta Abdulwahab Abubakar Goni Bauchi, shugaban Dr. Abdulwahab Abubakar Herbal and Islamic Clinic da ke Bauchi

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mutane 10 Da Ake Zargi Da Aikata Laifuka A Jigawa 

Ya zargi mutanen da yin amfani da sunansa, hoton kasuwancinsa da karatunsa wajen tallata tare da sayar da jabun magunguna. Wasu kuma a na zargin sun karɓi kuɗin jama’a da sunansa ba tare da kai musu magungunan da su ka saya ba.

Mutanen da a ka kama sun haɗa da Muhammad Usman, Husaini Kabir, Hassan Kabir, Suleiman Salihu da Nura Garba.

Rundunar ta ce a na ci gaba da bincike domin gano wasu mutanen da ke da hannu a lamarin.

Advertisement

Ta kuma gargadi jama’a da su tabbatar da sahihancin magunguna masu sayarwa da hanyoyin biyan kuɗi kafin yin mu’amala, musamman a kafafen sa da zumunta.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending