Connect with us

News

Buhari na halartar taron APC kan jadawalin zaɓen fid da gwani

Published

on

Daga mujahid danlami garba

 

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na halartar taron Majalisar Zartarwa na jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar da ke gudana yanzu haka.

Ana gudanar da taron ne a otel ɗin Transcop Hilton da ke Abuja karon farko tun bayan da APC ta zaɓi sabbin shugabanninta a watan Maris.

Ana sa ran ‘yan majalisar wanda Buhari na ɗaya daga cikinsu, za su daddale jadawalin zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar a matakin shugaban ƙasa da kuma na jihohi.

Za mu kawo ƙarin bayani da zarar mun samu…

Advertisement

Social embed from twitter

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending