News
Sha’aban Sharada ya garzaya kotu domin canja Gawuna
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Dan majalisar wakilai ta kasa na yankin karamar hukumar Birni daga jihar Kano, kuma shugaban kwamitin tsaro na majalisa, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya garzaya babbar kotun tarayya dake zamanta a Kano, yana kalubalantar dan takarar gwamnan Kano da jam’iyyar APC ta tsayar, mataimakin gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC.
Sha’aban Sharada ta bakin lauyansa, Barista J.O Asoluka SAN, yace tsayar da Gawuna yaci karo da sashi na 84 (1),(3),(8),(12) da kuma (13) cikin baka da dokar zaɓe wacce aka yiwa gyara, domin masu rike da mukaman siyasa sun kada kuri’a a zaɓen fidda gwani, wanda kuma sashi na 84(13) ya soke damar haka, kamar yadda jaridar Solacebace ta rawaito.
Gawuna dai shi ne wanda jam’iyyar APC ta tsayar domin yi mata takarar gwamnan Kano a zaben shekarar 2023 mai zuwa, wanda ya kayar da abokin karawarsa, Sha’aban Ibrahim Sharada.
Karin bayani nanan tafe…
